Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Facebook X (Twitter) Instagram
    ANZO WAJEN
    Advertise With Us
    Thursday, December 18
    • Shafin Farko
    • Labarai
    • Yanayi
    • Noma

      Kanfanin Dangote Ya Hada Gwiwa Da Abokan Huddarsa Don Bunkasa Noma

      November 25, 2025
    • Ma’adinai
    • Shari’a
    • Siyasa
    • Tattalin Arziki

      FIDAC Ta Bukaci Kungiyoyin Fararen Hula Su wayar da kan Jamaa akan Sauye-Sauyen Haraji na shekarar 2025 a Najeriya

      December 17, 2025
    • Karin Wasu
      1. Addini
      2. Aikata Laifuka
      3. Al’adu
      4. Harkokin Lafiya
      5. Harkokin Tsaro
      6. Harkokin Waje
      7. Ilimi
      8. Jirwaye
      9. Kimiyya Da Fasaha
      10. Kowane Labari
      11. Kwadago
      12. Nishani
      13. Ra’ayi
      14. Rubutun Zube
      15. Sufuri
      16. Yawon Bude Idanu
      17. Wasanni
      18. View All

      Karin Maganarmu Na Yau

      November 15, 2025

      Kwararren Likita Ya Shawarci “Yan Jarida Kan Lafiyar Kwakwalwa

      November 16, 2025

      An Kammala Taron Sanin Makamar Aiki Na Wakilan Kafafan Yada Labarai Na Jihar Kano A Kaduna

      November 16, 2025

      Kanfanin Dangote Ya Hada Gwiwa Da Kamfanin Honeywell Don Fadada Matatar Mai

      November 26, 2025

      Muna Gabatar Da Sabuwar Jaridarmu Ta Hausa Mai Suna: An zo wajen

      November 14, 2025

      Kuncin Rayuwa, Ya Hana Samari Aure

      November 15, 2025

      Aikin Wucin Gadi: Babban Barazana Ga Ci Gaban Dan Adam

      November 15, 2025
    ANZO WAJEN
    Home » Taron UNFPA Kan Ingantattun Halayen Maza Ya Kammala Da Shirye-Shiryen Aiki Kan kawar da Aurar da Ƙananan Yara, Kaciya Ga Mata( FGM )da tauye hankkin jinsi (SGBV)*
    Featured

    Taron UNFPA Kan Ingantattun Halayen Maza Ya Kammala Da Shirye-Shiryen Aiki Kan kawar da Aurar da Ƙananan Yara, Kaciya Ga Mata( FGM )da tauye hankkin jinsi (SGBV)*

    Abbas IbrahimBy Abbas IbrahimDecember 11, 2025No Comments6 Views
    IMG 20251210 WA0183

    IMG 20251210 WA0091(1) IMG 20251211 WA0072

    An kammala taron kwana huɗu da asusu majalisar dinkin duniya (UNFPA) ta shirya a hotel din Tahir dake garin kano, kan inganta kyawawan halayen maza, inda mahalarta suka ƙirƙiro tsare-tsare na ayyuka domin magance aurar da ƙananan yara, kaciya ga mata (FGM), da kuma cin zarafin jima’i da na jinsi (SGBV).

    IMG 20251211 WA0073(1)

    Mahalarta taron, waɗanda suka fito daga kungiyoyin matasa da na al’umma daban-daban, ana sa ran za su fara aiwatar da ayyukan da aka tsara kafin 31 ga watan Disambar shekarar ta 2025.

    IMG 20251211 WA0040(1)

    Da take jawabi a Yayin rufe taron, jami’ar UNFPA Hajiya Bahijja Bello Garko ta tabbatar da kudirin hukumar na ci gaba da yaƙi da matsalolin zamantakewa ta hanyar inganta kyawawan halayen maza.

    IMG 20251211 WA0039

    Ta ce an zaɓi mahalarta taron a matsayin manyan masu horaswa ne bisa cancanta da kuma aikin su na baya, inda ta nuna cikakkiyar gamsuwa da yadda za su iya aiwatar da abin da suka koya.

    IMG 20251210 WA0104(1)

    Hajiya Bahijja ta yaba da jajircewar da mahalartan suka nuna tsawon lokacin taron, tana mai cewa an shirya taron ne domin ƙara musu ƙwarewa wajen jagorantar wayar-da-kai a cikin al’ummominsu.

    IMG 20251210 WA0139

    Ta kuma tunatar da su muhimmancin kula da al’ada da dabi’un al’umma yayin yin aikin wayar-da-kai domin gujewa kin karbar abinda suka zo dashi

    A nata jawabin, Hajiya Karima Bungudu ta yi Karin gaske, a kan illolin munanan halayen maza ga cigaban al’umma, tana mai jaddada bukatar mayar da hankali wajen canza tunani da dabi’un da ke haifar da wariya da tashin hankali.

    Ta shawarci mahalarta taron, da su ci gaba da mayar da hankali yayin yada horon a garuruwansu.

    Masu gabatar da darussa, Dr. Olusegun Medupin da Dr. Auwalu Hallilu, sun jagoranci zaman rubuta rahoto, da Samar da hanyar kuɗaɗen gudanar da aiki, da illolin halayen maza marasa kyau ga jama’a.

    Da yawa daga cikin mahalartan sun bayyana taron a matsayin mai tasiri kuma mai sauya tunani, inda suka gode wa malamai bisa zurfin ilimi, da yadda suka gudanar da darussa cikin fasaha, da kuma jajircewarsu wajen gina sabuwar al’umma masu rajin daidaito tsakanin jinsi.

    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Abbas Ibrahim

      Related Posts

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      December 17, 2025

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      December 16, 2025

      Gidauniyar Bashir Da UNFPA Sun Koyawa Mata 25 Sana,oi A Gusau

      December 15, 2025
      Leave A Reply Cancel Reply

      Top Posts

      Daruruwan Mutane Sun Halarci Jana’izar Ado Lamco, a fadar masarautar Kano

      November 22, 202517

      Kimanin Mata Miliyan 68  Sun Fuskanci Shayi A Najeriya .

      December 10, 202511

      Muna Gabatar Da Sabuwar Jaridarmu Ta Hausa Mai Suna: An zo wajen

      November 14, 202511

      KARIN MAGANARMU NA YAU

      December 8, 20258
      Connect With Us
      • Facebook
      • Twitter
      • Instagram
      • YouTube
      • LinkedIn
      • TikTok
      • Telegram
      • WhatsApp
      Don't Miss
      Tattalin Arziki

      FIDAC Ta Bukaci Kungiyoyin Fararen Hula Su wayar da kan Jamaa akan Sauye-Sauyen Haraji na shekarar 2025 a Najeriya

      By Abbas IbrahimDecember 17, 2025

      Kungiyar tabbatar da da,a da daidaito akan al’amuran kudade da cigaban Al umma wato…

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      December 17, 2025

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      December 16, 2025

      Gidauniyar Bashir Da UNFPA Sun Koyawa Mata 25 Sana,oi A Gusau

      December 15, 2025
      © 2025 ANZO WAJEN. Developed by: ENGRMKS & CO.
      • Home
      • About Us
      • Advertise With Us
      • Contact Us
      • Disclaimer
      • Privacy Policy

      Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.