Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Facebook X (Twitter) Instagram
    ANZO WAJEN
    Advertise With Us
    Friday, December 19
    • Shafin Farko
    • Labarai
    • Yanayi
    • Noma

      Kanfanin Dangote Ya Hada Gwiwa Da Abokan Huddarsa Don Bunkasa Noma

      November 25, 2025
    • Ma’adinai
    • Shari’a
    • Siyasa
    • Tattalin Arziki

      FIDAC Ta Bukaci Kungiyoyin Fararen Hula Su wayar da kan Jamaa akan Sauye-Sauyen Haraji na shekarar 2025 a Najeriya

      December 17, 2025
    • Karin Wasu
      1. Addini
      2. Aikata Laifuka
      3. Al’adu
      4. Harkokin Lafiya
      5. Harkokin Tsaro
      6. Harkokin Waje
      7. Ilimi
      8. Jirwaye
      9. Kimiyya Da Fasaha
      10. Kowane Labari
      11. Kwadago
      12. Nishani
      13. Ra’ayi
      14. Rubutun Zube
      15. Sufuri
      16. Yawon Bude Idanu
      17. Wasanni
      18. View All

      Karin Maganarmu Na Yau

      November 15, 2025

      Kwararren Likita Ya Shawarci “Yan Jarida Kan Lafiyar Kwakwalwa

      November 16, 2025

      An Kammala Taron Sanin Makamar Aiki Na Wakilan Kafafan Yada Labarai Na Jihar Kano A Kaduna

      November 16, 2025

      Kanfanin Dangote Ya Hada Gwiwa Da Kamfanin Honeywell Don Fadada Matatar Mai

      November 26, 2025

      Muna Gabatar Da Sabuwar Jaridarmu Ta Hausa Mai Suna: An zo wajen

      November 14, 2025

      Kuncin Rayuwa, Ya Hana Samari Aure

      November 15, 2025

      Aikin Wucin Gadi: Babban Barazana Ga Ci Gaban Dan Adam

      November 15, 2025
    ANZO WAJEN
    Home » Rasuwar Ado Lamco Ta Girgiza Al,umma– Musa Kawu Wanzami
    Featured

    Rasuwar Ado Lamco Ta Girgiza Al,umma– Musa Kawu Wanzami

    Abbas IbrahimBy Abbas IbrahimNovember 23, 2025No Comments7 Views
    IMG 20251123 WA0227

     

    IMG 20251123 WA0232
    Shahararren Wanzami, Alhaji Musa Kawu Wanzami, ya bayyana rasuwar ɗan kasuwar Kano, Alhaji Ado Aminu (Mai Shinkafa), wanda aka fi sani da Alhaji Ado Lamco, a matsayin babban rashi da ya bar gibi mai wahalar cikewa.

    Alhaji Musa Wanzami, wanda ke gudanar da harkokinsa kusa da Lamco Pharmacy da ke kusa da Asibitin Koyarwa na Aminu Kano (AKTH), ya ce ya shafe fiye da shekaru 20 yana tare da marigayin. Ya bayyana Alhaji Ado a matsayin mutum mai karamci, sauƙin kai da tausayi, wanda ya taɓa rayuwar mutane da dama ta hanyar ayyukan alheri.

    A cewarsa, Alhaji Ado Lamco ya rayu rayuwa abin koyi, kullum a shirye yake ya tallafa wa marasa ƙarfin hali da kuma inganta walwalar mutanen da ke kewaye da shi.

    IMG 20251122 WA0205

    Wani maƙwabcin marigayin shima na tsawon shekaru 20 , Malam Inusa Mai Lemo, wanda ya zauna a yankin tun lokacin da aka kafa kantin maganin, ya kuma tuna yadda marigayin yake tsayawa tsayin daka wajen tallafa wa masu buƙata. Malam Inusa, da ke sana’arsa a gaban masallacin da Alhaji Ado ya gina, ya ce Jama,a na amfani da masallacin, inda suke tabbatar da kirkin mamacin.

    IMG 20251123 WA0296

    Dukkaninsu sun yi addu’a ga Allah Ya jikansa, Ya yi mashi gafara ya kuma baiwa iyalansa juriya wannan babban rashi.

    Alhaji Ado Lamco, mai shekaru 70, ya rasu ne a ranar Litinin, 17 ga Nuwamba, a wani asibiti da ke birnin Cairo, a masar, inda yake karɓar magani. Marigayin ɗan kasuwa , a fannin kiwon lafiya, ya bar ’ya’ya 15 — maza 10 da mata 5.

    An gudanar da sallar jana’izarsa ƙarƙashin jagorancin Sarkin Kano, Alhaji Muhammadu Sanusi II, inda daruruwan mutane suka halarta suka kuma raka gawarsa zuwa makabartar Dandolo, inda aka yi mashi sutura cikin hawaye da alhini daga iyalai, abokai, ’yan kasuwa da al’ummar yankin.

    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Abbas Ibrahim

      Related Posts

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      December 17, 2025

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      December 16, 2025

      Gidauniyar Bashir Da UNFPA Sun Koyawa Mata 25 Sana,oi A Gusau

      December 15, 2025
      Leave A Reply Cancel Reply

      Top Posts

      Daruruwan Mutane Sun Halarci Jana’izar Ado Lamco, a fadar masarautar Kano

      November 22, 202517

      Kimanin Mata Miliyan 68  Sun Fuskanci Shayi A Najeriya .

      December 10, 202511

      Muna Gabatar Da Sabuwar Jaridarmu Ta Hausa Mai Suna: An zo wajen

      November 14, 202511

      KARIN MAGANARMU NA YAU

      December 8, 20258
      Connect With Us
      • Facebook
      • Twitter
      • Instagram
      • YouTube
      • LinkedIn
      • TikTok
      • Telegram
      • WhatsApp
      Don't Miss
      Tattalin Arziki

      FIDAC Ta Bukaci Kungiyoyin Fararen Hula Su wayar da kan Jamaa akan Sauye-Sauyen Haraji na shekarar 2025 a Najeriya

      By Abbas IbrahimDecember 17, 2025

      Kungiyar tabbatar da da,a da daidaito akan al’amuran kudade da cigaban Al umma wato…

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      December 17, 2025

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      December 16, 2025

      Gidauniyar Bashir Da UNFPA Sun Koyawa Mata 25 Sana,oi A Gusau

      December 15, 2025
      © 2025 ANZO WAJEN. Developed by: ENGRMKS & CO.
      • Home
      • About Us
      • Advertise With Us
      • Contact Us
      • Disclaimer
      • Privacy Policy

      Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.