Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Facebook X (Twitter) Instagram
    ANZO WAJEN
    Advertise With Us
    Thursday, December 18
    • Shafin Farko
    • Labarai
    • Yanayi
    • Noma

      Kanfanin Dangote Ya Hada Gwiwa Da Abokan Huddarsa Don Bunkasa Noma

      November 25, 2025
    • Ma’adinai
    • Shari’a
    • Siyasa
    • Tattalin Arziki

      FIDAC Ta Bukaci Kungiyoyin Fararen Hula Su wayar da kan Jamaa akan Sauye-Sauyen Haraji na shekarar 2025 a Najeriya

      December 17, 2025
    • Karin Wasu
      1. Addini
      2. Aikata Laifuka
      3. Al’adu
      4. Harkokin Lafiya
      5. Harkokin Tsaro
      6. Harkokin Waje
      7. Ilimi
      8. Jirwaye
      9. Kimiyya Da Fasaha
      10. Kowane Labari
      11. Kwadago
      12. Nishani
      13. Ra’ayi
      14. Rubutun Zube
      15. Sufuri
      16. Yawon Bude Idanu
      17. Wasanni
      18. View All

      Karin Maganarmu Na Yau

      November 15, 2025

      Kwararren Likita Ya Shawarci “Yan Jarida Kan Lafiyar Kwakwalwa

      November 16, 2025

      An Kammala Taron Sanin Makamar Aiki Na Wakilan Kafafan Yada Labarai Na Jihar Kano A Kaduna

      November 16, 2025

      Kanfanin Dangote Ya Hada Gwiwa Da Kamfanin Honeywell Don Fadada Matatar Mai

      November 26, 2025

      Muna Gabatar Da Sabuwar Jaridarmu Ta Hausa Mai Suna: An zo wajen

      November 14, 2025

      Kuncin Rayuwa, Ya Hana Samari Aure

      November 15, 2025

      Aikin Wucin Gadi: Babban Barazana Ga Ci Gaban Dan Adam

      November 15, 2025
    ANZO WAJEN
    Home » Kwararren Likita Ya Shawarci “Yan Jarida Kan Lafiyar Kwakwalwa
    Harkokin Lafiya

    Kwararren Likita Ya Shawarci “Yan Jarida Kan Lafiyar Kwakwalwa

    Abdullahi YusufBy Abdullahi YusufNovember 16, 2025No Comments1 Views
    IMG 20251116 WA0011

    Kwararren Likita Ya Shawarci “Yan Jarida Kan Lafiyar Kwakwalwa

    Daga Abdullahi Yusuf

    Wani kwararren Likitan kula da Lafiyar Kwakwalwa,Dr. Aminu Ibrahim Shehu, ya shawarci “Yan Jarida da su rika lura da lafiyar kwakwalwarsu sosai, domin cigaban aikinsu.

    Dr.Aminu Ibrahim Shehu,wanda ke aiki a Asibitin Koyarwa na Mallam Aminu Kano da ke Kano,wato AKTH,ya ce hakan ya zamo dole,in an yi la’akari da yawan samun korafe-korafen galabaita da damuwar kwakwalwa a tsakanin “Yan Jarida.

    Ya ba da wannan shawarar ne a yayin da ya ke gabatar da wata Makala a kan galabaita da damuwar da “Yan Jarida ke fuskanta yayin gudanar da aikinsu,a wani taron Sanin Makamar Aiki da Kungiyar Wakilan Kafafan Yada Labarai Na Jihar Kano,wato(Correspondents’ Chapel),ta shirya domin “Ya “Yanta,wanda ke gudana a garin Kaduna,a halin yanzu.

    Ya ce, “Yan Jarida,kullum su na cikin gaggawar hada labaru don su buga su domin amfanin Jama’a,wanda shi ke sanyawa su ke galabaita da samun damuwa a kwakwalwarsu.

    Kwararren Likitan ya ce,ya kuma lura cewa,”Yan Jarida,kamar masu aikin Soja su ke,inda su kan ga abubuwan ban tsoro yayin da su ke gudanar da aikinsu.

    Ya ce, wannan al’amarin ma ya kan sanya su samu damuwa kwarai da gaske,wanda kuma ya ka iya tauye aikinsu.

    Saboda haka,tilas ne,in ji Dr.Shehu, “Yan Jarida su rika kula da lafiyar kwakwalwarsu sosai, in ba haka ba, a na iya samun raguwar masu Aikin Jarida saboda matsalolin da su ka shafi ciwon damuwa, har ma da kashe kai.

    Daga karshe, kwararren Likitan ya shawarci “Yan Jaridar da su rika kula da lafiyar jikinsu,ciki har da yin barci isasshe,su kuma rika neman taimakon kwararrun Likitoci yayin da duk su ka shiga cikin mummunar galabaita da damuwa.

    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Abdullahi Yusuf

      Leave A Reply Cancel Reply

      Top Posts

      Daruruwan Mutane Sun Halarci Jana’izar Ado Lamco, a fadar masarautar Kano

      November 22, 202517

      Kimanin Mata Miliyan 68  Sun Fuskanci Shayi A Najeriya .

      December 10, 202511

      Muna Gabatar Da Sabuwar Jaridarmu Ta Hausa Mai Suna: An zo wajen

      November 14, 202511

      KARIN MAGANARMU NA YAU

      December 8, 20258
      Connect With Us
      • Facebook
      • Twitter
      • Instagram
      • YouTube
      • LinkedIn
      • TikTok
      • Telegram
      • WhatsApp
      Don't Miss
      Tattalin Arziki

      FIDAC Ta Bukaci Kungiyoyin Fararen Hula Su wayar da kan Jamaa akan Sauye-Sauyen Haraji na shekarar 2025 a Najeriya

      By Abbas IbrahimDecember 17, 2025

      Kungiyar tabbatar da da,a da daidaito akan al’amuran kudade da cigaban Al umma wato…

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      December 17, 2025

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      December 16, 2025

      Gidauniyar Bashir Da UNFPA Sun Koyawa Mata 25 Sana,oi A Gusau

      December 15, 2025
      © 2025 ANZO WAJEN. Developed by: ENGRMKS & CO.
      • Home
      • About Us
      • Advertise With Us
      • Contact Us
      • Disclaimer
      • Privacy Policy

      Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.