Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Facebook X (Twitter) Instagram
    ANZO WAJEN
    Advertise With Us
    Thursday, December 18
    • Shafin Farko
    • Labarai
    • Yanayi
    • Noma

      Kanfanin Dangote Ya Hada Gwiwa Da Abokan Huddarsa Don Bunkasa Noma

      November 25, 2025
    • Ma’adinai
    • Shari’a
    • Siyasa
    • Tattalin Arziki

      FIDAC Ta Bukaci Kungiyoyin Fararen Hula Su wayar da kan Jamaa akan Sauye-Sauyen Haraji na shekarar 2025 a Najeriya

      December 17, 2025
    • Karin Wasu
      1. Addini
      2. Aikata Laifuka
      3. Al’adu
      4. Harkokin Lafiya
      5. Harkokin Tsaro
      6. Harkokin Waje
      7. Ilimi
      8. Jirwaye
      9. Kimiyya Da Fasaha
      10. Kowane Labari
      11. Kwadago
      12. Nishani
      13. Ra’ayi
      14. Rubutun Zube
      15. Sufuri
      16. Yawon Bude Idanu
      17. Wasanni
      18. View All

      Karin Maganarmu Na Yau

      November 15, 2025

      Kwararren Likita Ya Shawarci “Yan Jarida Kan Lafiyar Kwakwalwa

      November 16, 2025

      An Kammala Taron Sanin Makamar Aiki Na Wakilan Kafafan Yada Labarai Na Jihar Kano A Kaduna

      November 16, 2025

      Kanfanin Dangote Ya Hada Gwiwa Da Kamfanin Honeywell Don Fadada Matatar Mai

      November 26, 2025

      Muna Gabatar Da Sabuwar Jaridarmu Ta Hausa Mai Suna: An zo wajen

      November 14, 2025

      Kuncin Rayuwa, Ya Hana Samari Aure

      November 15, 2025

      Aikin Wucin Gadi: Babban Barazana Ga Ci Gaban Dan Adam

      November 15, 2025
    ANZO WAJEN
    Home » Kuncin Rayuwa, Ya Hana Samari Aure
    Featured

    Kuncin Rayuwa, Ya Hana Samari Aure

    Abdullahi YusufBy Abdullahi YusufNovember 15, 2025Updated:November 15, 2025No Comments8 Views
    Kuncin Rayuwa, Ya Hana Samari Aure

    Kuncin Rayuwa Ya Hana Samari Aure

    Daga Abdullahi Yusuf

    An ce, “Aure Yakin Mata.” Yanzu an wuce wannan wurin.Yanzu Aure ya zama “Yakin Maza,” domin kuwa a halin yanzu, Aure ya gagari Mazaje da dama, musamman ma “Samari “Yan Lalle.”

    Abin damuwa da takaici ne halin da Samari su ka shiga a kasar Hausa na rashin sukunin yin Aure.Yanzu Samari a wannan shiyya ta mu ta Arewa, musamman a garuruwanmu na Hausawa, ga su nan a yashe,sun balaga,sun kai,sun kawo,su na matukar bukatar Aure,amma babu hali.

    Yawancinsu sun yi karatun Boko sun gama,wadansu a cikinsu ma sun hadu da “Yanmata tun a Makaranta,sun yi soyayya har sun rabu.Yanzu sun dawo cikin unguwanninsu sun hadu da wadansu “Yanmatan sun sake bude wani sabon Babin na soyayya,amma duk ba halin yin Aure.

    Binciken da wannan Sabuwar Jarida, Anzowajen, ta yi, ya gano dalilai masu kwari da su ka hana wadannan Bayin Allah sukunin yin Aure.

    Daga cikinsu akwai Rashin Aikin Yi.Binciken ya gano cewa, yawancin wadannan Samari ba su da aikin yi, kuma da yawansu sun ki su yi Sana’a,wai su na jiran Aikin Ofis.Haka ne ya sa su ka rasa kudin da za su nemi Aure da su.

    Wadansun su kuma sun tsorata ne da tsadar da Aure ya ke da ita a halin yanzu, musamman akwatunan Aure,kama wajen taron biki da kama Amarya.Shi ya sa irin wadannan Samari su ke yin baya-baya da Aure.

    Rashin Mahalli da tsadar kudin haya su ma su na hana Samari yin Aure,domin hidimomin biki daban,sannan kuma fafutukar neman wajen da za a ajiye Amaryar daban.

    Wadannan matsalolin su su ka sanya yawancin Samarinmu a kasar Hausa su ka ma hakura da Auren,su ka mayar da al’amarinsu ga Allah(SWT) ta hanyar yin Azumi da sauransu.

    Wannan hali da Samarin su ka shiga,ba karamar matsala ba ce,domin kuwa Abu ne mai hadari ga Al’umma a ce ga tarin Samari kuma balagaggu a cikinta,ba su da Aure, kuma ba su da ranar yinsa.

    “Yar sa’ar da a ka yi kawai ita ce, yawancin Samarin su na sha’awar kallon Kwallon Kafa, wadansu ma a cikinsu su na buga Kwallon.Wannan harkar ta kan dauke musu hankali daga son mata.Allah Ya kawo mana dauki,amin.

     

    Kuncin Rayuwa Samari Aure Ya Hana
    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Abdullahi Yusuf

      Related Posts

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      December 17, 2025

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      December 16, 2025

      Gidauniyar Bashir Da UNFPA Sun Koyawa Mata 25 Sana,oi A Gusau

      December 15, 2025
      Leave A Reply Cancel Reply

      Top Posts

      Daruruwan Mutane Sun Halarci Jana’izar Ado Lamco, a fadar masarautar Kano

      November 22, 202517

      Kimanin Mata Miliyan 68  Sun Fuskanci Shayi A Najeriya .

      December 10, 202511

      Muna Gabatar Da Sabuwar Jaridarmu Ta Hausa Mai Suna: An zo wajen

      November 14, 202511

      KARIN MAGANARMU NA YAU

      December 8, 20258
      Connect With Us
      • Facebook
      • Twitter
      • Instagram
      • YouTube
      • LinkedIn
      • TikTok
      • Telegram
      • WhatsApp
      Don't Miss
      Tattalin Arziki

      FIDAC Ta Bukaci Kungiyoyin Fararen Hula Su wayar da kan Jamaa akan Sauye-Sauyen Haraji na shekarar 2025 a Najeriya

      By Abbas IbrahimDecember 17, 2025

      Kungiyar tabbatar da da,a da daidaito akan al’amuran kudade da cigaban Al umma wato…

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      December 17, 2025

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      December 16, 2025

      Gidauniyar Bashir Da UNFPA Sun Koyawa Mata 25 Sana,oi A Gusau

      December 15, 2025
      © 2025 ANZO WAJEN. Developed by: ENGRMKS & CO.
      • Home
      • About Us
      • Advertise With Us
      • Contact Us
      • Disclaimer
      • Privacy Policy

      Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.