Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Facebook X (Twitter) Instagram
    ANZO WAJEN
    Advertise With Us
    Thursday, December 18
    • Shafin Farko
    • Labarai
    • Yanayi
    • Noma

      Kanfanin Dangote Ya Hada Gwiwa Da Abokan Huddarsa Don Bunkasa Noma

      November 25, 2025
    • Ma’adinai
    • Shari’a
    • Siyasa
    • Tattalin Arziki

      FIDAC Ta Bukaci Kungiyoyin Fararen Hula Su wayar da kan Jamaa akan Sauye-Sauyen Haraji na shekarar 2025 a Najeriya

      December 17, 2025
    • Karin Wasu
      1. Addini
      2. Aikata Laifuka
      3. Al’adu
      4. Harkokin Lafiya
      5. Harkokin Tsaro
      6. Harkokin Waje
      7. Ilimi
      8. Jirwaye
      9. Kimiyya Da Fasaha
      10. Kowane Labari
      11. Kwadago
      12. Nishani
      13. Ra’ayi
      14. Rubutun Zube
      15. Sufuri
      16. Yawon Bude Idanu
      17. Wasanni
      18. View All

      Karin Maganarmu Na Yau

      November 15, 2025

      Kwararren Likita Ya Shawarci “Yan Jarida Kan Lafiyar Kwakwalwa

      November 16, 2025

      An Kammala Taron Sanin Makamar Aiki Na Wakilan Kafafan Yada Labarai Na Jihar Kano A Kaduna

      November 16, 2025

      Kanfanin Dangote Ya Hada Gwiwa Da Kamfanin Honeywell Don Fadada Matatar Mai

      November 26, 2025

      Muna Gabatar Da Sabuwar Jaridarmu Ta Hausa Mai Suna: An zo wajen

      November 14, 2025

      Kuncin Rayuwa, Ya Hana Samari Aure

      November 15, 2025

      Aikin Wucin Gadi: Babban Barazana Ga Ci Gaban Dan Adam

      November 15, 2025
    ANZO WAJEN
    Home » Kanfanin Dangote Ya Hada Gwiwa Da Abokan Huddarsa Don Bunkasa Noma
    Featured

    Kanfanin Dangote Ya Hada Gwiwa Da Abokan Huddarsa Don Bunkasa Noma

    Abdullahi YusufBy Abdullahi YusufNovember 25, 2025Updated:November 25, 2025No Comments6 Views
    IMG 20251124 WA0264

    Kanfanin Dangote Ya Hada Gwiwa Da Abokan Huddarsa Don Bunkasa Noma

    Daga Abdullahi Yusuf

    Shahararren kanfanin nan na Dangote Group ya hada gwiwa da abokan huddarsa domin bunkasa harkokin noma a Nigeria.

    Wata sanarwa wadda mai magana da yawun kanfanin,Anthony Chiejina, ya sanya wa hannu, tace wannan yunkuri ya zo ne daidai lokacin da kanfanin ya dauki nauyin Bikin Nuna Fasahar Noma Na Kasa, karo na sha bakwai, wanda a ke farawa a birnin Keffi da ke cikin Jihar Nasarawa, a yau Talata,25 ga watan Nuwamba.

    Chiejina ya ce bunkasa aikin noma ta hanyar amfani da na’urorin zamani zai bunkasa arzikin kasa,ya kuma samar da aikin yi ga matasan Nigeria.

    Ta hanyar wannan hadin gwiwa,in ji shi, kanfanin na Dangote ya ke kokarin bunkasa noman amfanin gona na sayarwa,domin bunkasa tattalin arzikin kasa.

    Ya ce taken wannan bikin na nuna fasahar noma na kasa shine,”Karfafawa Kananan Manoma Gwiwa Don Bunkasa Noma,” zai taimaka wajen samar da abinci ga “Yan Kasa.

    Ya ce idan har aka bunkasa noma,to za a bunkasa tattalin arkin kasa,samar da isasshen abinci da kuma aikin yi ga “Yan Kasa.

    Mai magana da yawun kanfanin Dangoten, ya kara da cewa bikin na nuna fasahar noma zai kuma daidaita lokutan aikin noma,da kuma samar da sabbin dabarun noma.

    Ya ce a halin yanzu, kanfanin na Dangote,ya na samar da masana’antun casa shinkafa a jihohin Kano, Jigawa, Niger, Kebbi, and Sokoto, wadanda za su iya casa shinkafa tan miliyan 1.5 a shekara.

    Ya ce wannan ya na daga cikin kokarin kanfanin na taimakawa Gwamnati wajen samar da isasshen abinci ga kasa.

    Daga nan sai sanarwar ta ambato babbar mai bai wa Shugaban gungun kamfanonin Dangote shawara,Fatima Wali-Abdurrahman, ta na cewa a cikin yunkurin kanfanin na sarrafa kayan gona a Nigeria, ya na zuba jari a bangaren samar da sukari a jihohin Nasarawa da Adamawa.

    Fatima ta kuma ce a yanzu haka, kanfanin na Dangote ya kafa kanfanin samar da takin zamani mai fitar da tan miliyan uku na taki,a Lekki Free Trade Zone da ke Jihar Lagos.

    Shugaban kwamitin amintattu na Kungiyar Bunkasa Noma ta kasa, wadda ita ce ta shirya bikin,Arc Kabiru Adamu, ya ce kanfanin Dangote babban abokin huddarsu ne da dadewa,wanda ya ke taimaka musu kwarai wajen shirya bikin.

    Arc Kabiru Adamu, wanda kuma shi ne Shugaban Kungiyar Manoma ta kasa,wato AFAN,ya yi kira ga kanfanin na Dangote da ya mayar da hankali wajen bunkasa noma,bayan da ya ci nasara a kasuwar mai da gas.

    Ya ce a na sa ran cewa bikin zai samu halartar manyan manoma, masana’antu,masu bincike,matasa da mata manoma,duka a cikin taimakonsu na bunkasa samar da abinci a cikin kasa.

     

    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Abdullahi Yusuf

      Related Posts

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      December 17, 2025

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      December 16, 2025

      Gidauniyar Bashir Da UNFPA Sun Koyawa Mata 25 Sana,oi A Gusau

      December 15, 2025
      Leave A Reply Cancel Reply

      Top Posts

      Daruruwan Mutane Sun Halarci Jana’izar Ado Lamco, a fadar masarautar Kano

      November 22, 202517

      Kimanin Mata Miliyan 68  Sun Fuskanci Shayi A Najeriya .

      December 10, 202511

      Muna Gabatar Da Sabuwar Jaridarmu Ta Hausa Mai Suna: An zo wajen

      November 14, 202511

      KARIN MAGANARMU NA YAU

      December 8, 20258
      Connect With Us
      • Facebook
      • Twitter
      • Instagram
      • YouTube
      • LinkedIn
      • TikTok
      • Telegram
      • WhatsApp
      Don't Miss
      Tattalin Arziki

      FIDAC Ta Bukaci Kungiyoyin Fararen Hula Su wayar da kan Jamaa akan Sauye-Sauyen Haraji na shekarar 2025 a Najeriya

      By Abbas IbrahimDecember 17, 2025

      Kungiyar tabbatar da da,a da daidaito akan al’amuran kudade da cigaban Al umma wato…

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      December 17, 2025

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      December 16, 2025

      Gidauniyar Bashir Da UNFPA Sun Koyawa Mata 25 Sana,oi A Gusau

      December 15, 2025
      © 2025 ANZO WAJEN. Developed by: ENGRMKS & CO.
      • Home
      • About Us
      • Advertise With Us
      • Contact Us
      • Disclaimer
      • Privacy Policy

      Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.