Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Facebook X (Twitter) Instagram
    ANZO WAJEN
    Advertise With Us
    Saturday, December 20
    • Shafin Farko
    • Labarai
    • Yanayi
    • Noma

      Kanfanin Dangote Ya Hada Gwiwa Da Abokan Huddarsa Don Bunkasa Noma

      November 25, 2025
    • Ma’adinai
    • Shari’a
    • Siyasa
    • Tattalin Arziki

      FIDAC Ta Bukaci Kungiyoyin Fararen Hula Su wayar da kan Jamaa akan Sauye-Sauyen Haraji na shekarar 2025 a Najeriya

      December 17, 2025
    • Karin Wasu
      1. Addini
      2. Aikata Laifuka
      3. Al’adu
      4. Harkokin Lafiya
      5. Harkokin Tsaro
      6. Harkokin Waje
      7. Ilimi
      8. Jirwaye
      9. Kimiyya Da Fasaha
      10. Kowane Labari
      11. Kwadago
      12. Nishani
      13. Ra’ayi
      14. Rubutun Zube
      15. Sufuri
      16. Yawon Bude Idanu
      17. Wasanni
      18. View All

      Karin Maganarmu Na Yau

      November 15, 2025

      Kwararren Likita Ya Shawarci “Yan Jarida Kan Lafiyar Kwakwalwa

      November 16, 2025

      An Kammala Taron Sanin Makamar Aiki Na Wakilan Kafafan Yada Labarai Na Jihar Kano A Kaduna

      November 16, 2025

      Kanfanin Dangote Ya Hada Gwiwa Da Kamfanin Honeywell Don Fadada Matatar Mai

      November 26, 2025

      Muna Gabatar Da Sabuwar Jaridarmu Ta Hausa Mai Suna: An zo wajen

      November 14, 2025

      Kuncin Rayuwa, Ya Hana Samari Aure

      November 15, 2025

      Aikin Wucin Gadi: Babban Barazana Ga Ci Gaban Dan Adam

      November 15, 2025
    ANZO WAJEN
    Home » Gwamna Abba Yusuf Ya Gabatar Da Kasafin Kudi Na N1.3trn Ga Majalisar Dokokin Jihar Kano
    Featured

    Gwamna Abba Yusuf Ya Gabatar Da Kasafin Kudi Na N1.3trn Ga Majalisar Dokokin Jihar Kano

    Abdullahi YusufBy Abdullahi YusufNovember 19, 2025No Comments1 Views
    IMG 20251119 WA0130

    Gwamna Abba Yusuf Ya Gabatar Da Kasafin Kudi Na N1.3trn Ga Majalisar Dokokin Jihar Kano

    Daga Abdullahi Yusuf

    Gwamna Abba Kabir Yusuf ya gabatar da kasafin kudi na N1.368 trillion na shekarar kudi ta 2026 ga Majalisar Dokokin Jihar Kano,a ranar Laraban nan.

    Kasafin kudin Mai taken,” Kasafin Kudi Na Gudanar Da Mahimman Ayyuka Da Cigaban Kasa Mai Dorewa,” wani shiri ne na kashe kudi domin gudanar da ayyukan raya kasa a duk fadin jhar,in ji Gwamnan.

    Ya ce Kasafin Kudin,an tsarashi ne domin kammala wasu manyan ayyukan da aka fara a duk fadin Jihar,tare da bullo da wasu sabbin tsare-tsare don bunkasa tattalin arzikin Jihar.

    Gwamnan ya ce an ware kaso mai tsoka daga cikin Kasafin Kudin domin gudanar da mahimman ayyuka kamar yadda a ka zayyana a cikin kudirin Gwamnatinsa na gudanar da manyan ayyuka da bunkasa ci gaban Jihar.

    Ya ce daga cikin kudin,an ware N934.640 billion domin gabatar da manyan ayyuka, yayin da za a kashe N433.487 billion domin ayyukan yau da kullum.

    Gwamnan ya kara da cewa, Kasafin Kudin ya na dauke da burin gudanar da ayyukan da za su bunkasa rayuwar mutanen Jihar,ciki har da gina hanyoyi,samar da ruwan sha,tsaro,tallafi da bunkasa birane.

    Saboda haka, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bukaci Majalisar Dokokin da ta duba da kuma amince da Kasafin Kudin a kan lokaci, domin a samu damar gudanar da ayyukan da ta kunsa a cikin shekarar kudi ta badi.

    Da ya ke mayar da jawabi, Shugaban Majalisar, Alhaji Jibril Fagore, ya gode wa Gwamnan saboda mulkin gaskiya da adalci
    da ya ke gudanarwa a Jihar,ya na mai ba shi tabbacin Majalisar na duba Kasafin Kudin cikin tsanaki kuma a kan lokaci.

    Falgore,ya kuma yabawa bangaren zartaswa na Jihar saboda akin da ta ke yi kafada-da-kafada da Majalisar domin ci gaban Jihar.

    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Abdullahi Yusuf

      Related Posts

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      December 17, 2025

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      December 16, 2025

      Gidauniyar Bashir Da UNFPA Sun Koyawa Mata 25 Sana,oi A Gusau

      December 15, 2025
      Leave A Reply Cancel Reply

      Top Posts

      Daruruwan Mutane Sun Halarci Jana’izar Ado Lamco, a fadar masarautar Kano

      November 22, 202517

      Kimanin Mata Miliyan 68  Sun Fuskanci Shayi A Najeriya .

      December 10, 202511

      Muna Gabatar Da Sabuwar Jaridarmu Ta Hausa Mai Suna: An zo wajen

      November 14, 202511

      KARIN MAGANARMU NA YAU

      December 8, 20258
      Connect With Us
      • Facebook
      • Twitter
      • Instagram
      • YouTube
      • LinkedIn
      • TikTok
      • Telegram
      • WhatsApp
      Don't Miss
      Tattalin Arziki

      FIDAC Ta Bukaci Kungiyoyin Fararen Hula Su wayar da kan Jamaa akan Sauye-Sauyen Haraji na shekarar 2025 a Najeriya

      By Abbas IbrahimDecember 17, 2025

      Kungiyar tabbatar da da,a da daidaito akan al’amuran kudade da cigaban Al umma wato…

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      December 17, 2025

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      December 16, 2025

      Gidauniyar Bashir Da UNFPA Sun Koyawa Mata 25 Sana,oi A Gusau

      December 15, 2025
      © 2025 ANZO WAJEN. Developed by: ENGRMKS & CO.
      • Home
      • About Us
      • Advertise With Us
      • Contact Us
      • Disclaimer
      • Privacy Policy

      Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.