Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Facebook X (Twitter) Instagram
    ANZO WAJEN
    Advertise With Us
    Thursday, December 18
    • Shafin Farko
    • Labarai
    • Yanayi
    • Noma

      Kanfanin Dangote Ya Hada Gwiwa Da Abokan Huddarsa Don Bunkasa Noma

      November 25, 2025
    • Ma’adinai
    • Shari’a
    • Siyasa
    • Tattalin Arziki

      FIDAC Ta Bukaci Kungiyoyin Fararen Hula Su wayar da kan Jamaa akan Sauye-Sauyen Haraji na shekarar 2025 a Najeriya

      December 17, 2025
    • Karin Wasu
      1. Addini
      2. Aikata Laifuka
      3. Al’adu
      4. Harkokin Lafiya
      5. Harkokin Tsaro
      6. Harkokin Waje
      7. Ilimi
      8. Jirwaye
      9. Kimiyya Da Fasaha
      10. Kowane Labari
      11. Kwadago
      12. Nishani
      13. Ra’ayi
      14. Rubutun Zube
      15. Sufuri
      16. Yawon Bude Idanu
      17. Wasanni
      18. View All

      Karin Maganarmu Na Yau

      November 15, 2025

      Kwararren Likita Ya Shawarci “Yan Jarida Kan Lafiyar Kwakwalwa

      November 16, 2025

      An Kammala Taron Sanin Makamar Aiki Na Wakilan Kafafan Yada Labarai Na Jihar Kano A Kaduna

      November 16, 2025

      Kanfanin Dangote Ya Hada Gwiwa Da Kamfanin Honeywell Don Fadada Matatar Mai

      November 26, 2025

      Muna Gabatar Da Sabuwar Jaridarmu Ta Hausa Mai Suna: An zo wajen

      November 14, 2025

      Kuncin Rayuwa, Ya Hana Samari Aure

      November 15, 2025

      Aikin Wucin Gadi: Babban Barazana Ga Ci Gaban Dan Adam

      November 15, 2025
    ANZO WAJEN
    Home » FIDAC Ta Bukaci Kungiyoyin Fararen Hula Su wayar da kan Jamaa akan Sauye-Sauyen Haraji na shekarar 2025 a Najeriya
    Tattalin Arziki

    FIDAC Ta Bukaci Kungiyoyin Fararen Hula Su wayar da kan Jamaa akan Sauye-Sauyen Haraji na shekarar 2025 a Najeriya

    Abbas IbrahimBy Abbas IbrahimDecember 17, 2025No Comments2 Views
    IMG 20251217 WA0028

     

    Kungiyar tabbatar da da,a da daidaito akan al’amuran kudade da cigaban Al umma wato Fiscal Discipline and Development Advocacy (FIDAC) ta yi kira ga kungiyoyin fararen hula (CSOs) da su bayar da muhimmiyar gidunmowa wajen tabbatar da aiwatar da Dokokin Sauye-sauyen Haraji na shekarar 2025 tana mai jaddada cewa nasara ba kawai a wayar da kai take ba akwai bukatar shigo da Al umma

    A cikin wata sanarwa da shugaban ta, Abdussalam Muhammad Kani, ya fitar ya bayyana sauye-sauyen harajin a matsayin wani mataki na zamanantarwa tare da inganta tsarin haraji na Najeriya,da kuma fadada hanyoyin samar da kudin shiga da kare masu karamin karfi, da kuma karfafa dangantaka tsakanin biyan harajin da ci gaban kasa.

    FIDAC ta ce tasirin wadannan sauye-sauyen zai dogara ne da fahimtar jama’a tare da amincewar su, da kuma bin doka da oda
    Kungiyar ta gargadi cewa tsarin sabbin dokokin na da rikitarwa wanda zai yi wahalar fahimta wajen jama’a idan ba a fassara musu su yadda ya dace ba.

    Kungiyar ta bukaci kungiyoyin fararen hula da su fassara sauye-sauyen yadda Al umma zasu fahimta ta hanyar wayar da kan al umma da shirye-shiryenabijin da kuma amfani da kafafen sada zumunta tare da hada kai da ‘yan kasuwa kanana da matsakaita da sauransu

    Daga cikin muhimman sauye-sauyen, FIDAC ta jaddada cewa wadanda ke samun kudin da basu haura naira ₦800,000 a shekara ba,ba za su biya haraji ba, yayin da kuma kananan ‘yan kasuwa za su amfana da tallafin kudin haya har zuwa ₦500,000.

    Yayin da Najeriya ke komawa tsarin haraji na zamani wato digital da suka hadar da e-invoicing da electronic filling

    FIDAC ta bukaci kungiyoyin fararen hula da su isar da sakon ta yanar gizo da kuma bayyana alfanunsa domin karfafawa Al umma.

    Ta kuma bukaci a samar da tallafi da saukakawa wajen yin rajistar TIN da sauran tsarukan haraji.

    FIDAC ta jaddada bukatar yin gaskiya da rikon amana, inda ta bukaci kungiyoyin fararen hula da su bukaci bayanai daga gwamnati kan yadda ake amfani da kudaden haraji da kuma sa ido kan yadda ake aiwatar da dokoki domin kare masu karamin karfi.

    FIDAC ta ce dokokin sauye-sauyen haraji na 2025 wata babbar dama ce ga kungiyoyin fararen hula wajen karfafa gwiwa da amincewa da tsarin haraji, domin hakan wani ginshiki ne da zai taimaka wajen ci gaban kasa.

    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Abbas Ibrahim

      Leave A Reply Cancel Reply

      Top Posts

      Daruruwan Mutane Sun Halarci Jana’izar Ado Lamco, a fadar masarautar Kano

      November 22, 202517

      Kimanin Mata Miliyan 68  Sun Fuskanci Shayi A Najeriya .

      December 10, 202511

      Muna Gabatar Da Sabuwar Jaridarmu Ta Hausa Mai Suna: An zo wajen

      November 14, 202511

      KARIN MAGANARMU NA YAU

      December 8, 20258
      Connect With Us
      • Facebook
      • Twitter
      • Instagram
      • YouTube
      • LinkedIn
      • TikTok
      • Telegram
      • WhatsApp
      Don't Miss
      Tattalin Arziki

      FIDAC Ta Bukaci Kungiyoyin Fararen Hula Su wayar da kan Jamaa akan Sauye-Sauyen Haraji na shekarar 2025 a Najeriya

      By Abbas IbrahimDecember 17, 2025

      Kungiyar tabbatar da da,a da daidaito akan al’amuran kudade da cigaban Al umma wato…

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      December 17, 2025

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      December 16, 2025

      Gidauniyar Bashir Da UNFPA Sun Koyawa Mata 25 Sana,oi A Gusau

      December 15, 2025
      © 2025 ANZO WAJEN. Developed by: ENGRMKS & CO.
      • Home
      • About Us
      • Advertise With Us
      • Contact Us
      • Disclaimer
      • Privacy Policy

      Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.