Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Facebook X (Twitter) Instagram
    ANZO WAJEN
    Advertise With Us
    Saturday, December 20
    • Shafin Farko
    • Labarai
    • Yanayi
    • Noma

      Kanfanin Dangote Ya Hada Gwiwa Da Abokan Huddarsa Don Bunkasa Noma

      November 25, 2025
    • Ma’adinai
    • Shari’a
    • Siyasa
    • Tattalin Arziki

      FIDAC Ta Bukaci Kungiyoyin Fararen Hula Su wayar da kan Jamaa akan Sauye-Sauyen Haraji na shekarar 2025 a Najeriya

      December 17, 2025
    • Karin Wasu
      1. Addini
      2. Aikata Laifuka
      3. Al’adu
      4. Harkokin Lafiya
      5. Harkokin Tsaro
      6. Harkokin Waje
      7. Ilimi
      8. Jirwaye
      9. Kimiyya Da Fasaha
      10. Kowane Labari
      11. Kwadago
      12. Nishani
      13. Ra’ayi
      14. Rubutun Zube
      15. Sufuri
      16. Yawon Bude Idanu
      17. Wasanni
      18. View All

      Karin Maganarmu Na Yau

      November 15, 2025

      Kwararren Likita Ya Shawarci “Yan Jarida Kan Lafiyar Kwakwalwa

      November 16, 2025

      An Kammala Taron Sanin Makamar Aiki Na Wakilan Kafafan Yada Labarai Na Jihar Kano A Kaduna

      November 16, 2025

      Kanfanin Dangote Ya Hada Gwiwa Da Kamfanin Honeywell Don Fadada Matatar Mai

      November 26, 2025

      Muna Gabatar Da Sabuwar Jaridarmu Ta Hausa Mai Suna: An zo wajen

      November 14, 2025

      Kuncin Rayuwa, Ya Hana Samari Aure

      November 15, 2025

      Aikin Wucin Gadi: Babban Barazana Ga Ci Gaban Dan Adam

      November 15, 2025
    ANZO WAJEN
    Home » Sarkin Kano Sunusi Ya Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Wadanda Harin “Yan Bindiga Ya Shafa A Garin Faruruwa
    Featured

    Sarkin Kano Sunusi Ya Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Wadanda Harin “Yan Bindiga Ya Shafa A Garin Faruruwa

    Abdullahi YusufBy Abdullahi YusufNovember 19, 2025No Comments1 Views
    images (63)

    Sarkin Kano Sunusi Ya Kai Ziyarar Ta’aziyya Ga Wadanda Harin “Yan Bindiga Ya Shafa A Garin Faruruwa

    By Abdullahi Yusuf

    Sarkin Kano,Khalipha Muhammadu Sanusi II,ya kai ziyarar ta’aziyya ga iyalai da kuma wadanda harin “Yan Bindiga ya rutsa da su a garin Faruruwa da ke cikin Karamar Hukumar Shanono, a kwanan baya.

    Wata sanarwa da Shugaban Ayarin “Yan Jarida masu dauko labarai daga Fadar Kano,Sadam Na’ando Yakasai,ya bayar,ta ce Sarkin ya yi ta’aziyya ga mutanen da harin ya shafa a garin na Faruruwa.

    Sanarwar tace yayin ziyarar, Sarkin ya yi addu’a ga Allah da ya jikan wadanda su ka rasu a sakamakon harin, ya kuma bai wa iyalan mamatan hakurin wannan rashi.

    Sarkin,ya kuma yi kira ga mazauna yankin na Shanono da su zama masu kaffa-kaffa tare da lura da yanayin tsaro a wannan shiyya,su kuma kai rahoton duk wani motsi da ba su yarda da shi ba ga jami’an tsaro domin a yi maganinsa nan take.

    Daga nan sai Sarkin ya yi kira ga mazauna yankin na Shanono da kuma mutanen Jihar Kano ba ki daya, da su yi ta addu’a domin samun zaman lafiya,kwanciyar hankali da hadin kai a Jihar Kano da Nigeria ba ki daya.

    A cikin jawabinsa yayin ziyarar,Hakimin Shanono kuma Dankadan Kano, Dr. Bashir Ibrahim Muhammad, ya gode wa Sarkin saboda wannan ziyara da ya kai,wadda ya ce nuni ce ga irin yadda ya damu da rayuwa da walwalar talakawansa.

    Dr.Bashir ya yi addu’a ga Allah da ya taimaki Sarki,ya kuma kara yi masa jagora wajen kokarin da ya ke yi na tafiyar da mulkin Kano.

    Shi ma a nasa jawabin, Shugaban Karamar Hukumar ta Shanono,Ahaji Barau Abubakar,ya jaddada kudirin Karamar Hukumar na ci gaba da daukar duk wasu matakai da su ka dace domin yin maganin matsalar tsaron da ta addabi yankin.

    Daga nan sai Shugaban Karamar Hukumar ya gode wa Gwamnatin Jihar Kano saboda irin kokarin da ta ke yi domin kawar da matsalar hare-haren “Yan Bindiga daga yankin.

    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Abdullahi Yusuf

      Related Posts

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      December 17, 2025

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      December 16, 2025

      Gidauniyar Bashir Da UNFPA Sun Koyawa Mata 25 Sana,oi A Gusau

      December 15, 2025
      Leave A Reply Cancel Reply

      Top Posts

      Daruruwan Mutane Sun Halarci Jana’izar Ado Lamco, a fadar masarautar Kano

      November 22, 202517

      Kimanin Mata Miliyan 68  Sun Fuskanci Shayi A Najeriya .

      December 10, 202511

      Muna Gabatar Da Sabuwar Jaridarmu Ta Hausa Mai Suna: An zo wajen

      November 14, 202511

      KARIN MAGANARMU NA YAU

      December 8, 20258
      Connect With Us
      • Facebook
      • Twitter
      • Instagram
      • YouTube
      • LinkedIn
      • TikTok
      • Telegram
      • WhatsApp
      Don't Miss
      Tattalin Arziki

      FIDAC Ta Bukaci Kungiyoyin Fararen Hula Su wayar da kan Jamaa akan Sauye-Sauyen Haraji na shekarar 2025 a Najeriya

      By Abbas IbrahimDecember 17, 2025

      Kungiyar tabbatar da da,a da daidaito akan al’amuran kudade da cigaban Al umma wato…

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      December 17, 2025

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      December 16, 2025

      Gidauniyar Bashir Da UNFPA Sun Koyawa Mata 25 Sana,oi A Gusau

      December 15, 2025
      © 2025 ANZO WAJEN. Developed by: ENGRMKS & CO.
      • Home
      • About Us
      • Advertise With Us
      • Contact Us
      • Disclaimer
      • Privacy Policy

      Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.