Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Facebook X (Twitter) Instagram
    ANZO WAJEN
    Advertise With Us
    Thursday, December 18
    • Shafin Farko
    • Labarai
    • Yanayi
    • Noma

      Kanfanin Dangote Ya Hada Gwiwa Da Abokan Huddarsa Don Bunkasa Noma

      November 25, 2025
    • Ma’adinai
    • Shari’a
    • Siyasa
    • Tattalin Arziki

      FIDAC Ta Bukaci Kungiyoyin Fararen Hula Su wayar da kan Jamaa akan Sauye-Sauyen Haraji na shekarar 2025 a Najeriya

      December 17, 2025
    • Karin Wasu
      1. Addini
      2. Aikata Laifuka
      3. Al’adu
      4. Harkokin Lafiya
      5. Harkokin Tsaro
      6. Harkokin Waje
      7. Ilimi
      8. Jirwaye
      9. Kimiyya Da Fasaha
      10. Kowane Labari
      11. Kwadago
      12. Nishani
      13. Ra’ayi
      14. Rubutun Zube
      15. Sufuri
      16. Yawon Bude Idanu
      17. Wasanni
      18. View All

      Karin Maganarmu Na Yau

      November 15, 2025

      Kwararren Likita Ya Shawarci “Yan Jarida Kan Lafiyar Kwakwalwa

      November 16, 2025

      An Kammala Taron Sanin Makamar Aiki Na Wakilan Kafafan Yada Labarai Na Jihar Kano A Kaduna

      November 16, 2025

      Kanfanin Dangote Ya Hada Gwiwa Da Kamfanin Honeywell Don Fadada Matatar Mai

      November 26, 2025

      Muna Gabatar Da Sabuwar Jaridarmu Ta Hausa Mai Suna: An zo wajen

      November 14, 2025

      Kuncin Rayuwa, Ya Hana Samari Aure

      November 15, 2025

      Aikin Wucin Gadi: Babban Barazana Ga Ci Gaban Dan Adam

      November 15, 2025
    ANZO WAJEN
    Home » An Kammala Taron Sanin Makamar Aiki Na Wakilan Kafafan Yada Labarai Na Jihar Kano A Kaduna
    Featured

    An Kammala Taron Sanin Makamar Aiki Na Wakilan Kafafan Yada Labarai Na Jihar Kano A Kaduna

    Abdullahi YusufBy Abdullahi YusufNovember 16, 2025No Comments2 Views
    IMG 20251115 WA0148(3)

    An Kammala Taron Sanin Makamar Aiki Na Wakilan Kafafan Yada Labarai Na Jihar Kano A Kaduna

    Daga Abdullahi Yusuf

    A yau,16 ga watan Nuwamba 2025, ne a ka kawo karshen taron Sanin Makamar Aiki na Kungiyar Wakilan Kafafan Yada Labarai Na Jihar Kano,wato Correspondents’ Chapel,a garin Kaduna.

    A lokacin taron na kwana biyu, masana sun gabatar da Makaloli dabam-dabam wadanda suka nusar da Wakilan hanyoyin da za su inganta aikinsu na rubutawa da buga labarai.

    Daga cikin Makalolin har da wadda Dr.Aminu Ibrahim Shehu,wanda ke aiki a Asibitin Koyarwa na Mallam Aminu Kano da ke Kano,wato AKTH, ya kawo, wadda ta koya wa Wakilan yadda za su kula da lafiyarsu yayinda su ke gudanar da aikinsu na rubutawa da buga labarai.

    Sai kuma Hajiya Sani,wata kwararriyar “Yar Jarida ce, wadda ta nusar da Wakilan game da shigowar Manhajar nan ta AI da kuma yadda za su rika amfani da ita wajen gudanar da aikinsu.

    Farfesa Sule Ya’u Sule na Jami’ar Bayero ta Kano,wato,BUK, shi ma ya gabatar da Makala wadda ta koya wa Wakilan yadda za su rika mu’amala da Gwamnatin Jihar Kano cikin sauki ba tare da aikinsu ya tawaya ba.

    Daga nan sai wani kwararren Dan Jarida,wato Alhaji Abdullateef Abubakar Jos,da kuma wani kwararren Lauya kuma Dan Jarida, Yusuf Abdulsalam, wadanda su ka koya wa Wakilan dabarun nemo labarai da wallafasu,ba tare da muzguna wa mutane ko bata musu suna ba.

    Gwamna Abba Kabir Yusuf ne ya bude taron,inda ya yabawa Wakilan kan yadda su ke yada sahihan labarai game da Gwamnati da mutanen Jihar Kano.

    Gwamnan,wanda Sakataren Gwamnatin Jiha, Alhaji Umar Farouk Ibrahim ya wakilta,ya ce Gwamnatinsa za ta ci gaba da tallafawa Wakilan ta hanyoyin da su ka dace,ta yadda za su ji dadin gudanar da aikinsu.

    A cikin jawabinsa na maraba,Shugaban Kungiyar Wakilan Kafafan Yada Labaran na Jihar Kano, Alhaji Murtala Adewale,ya ce an shirya taron ne domin a bai wa “Yan Kungiyar damar samun karin ilimin gudanar da aikinsu, sannan kuma su samu su sarara daga ruguntsumin nemo labarai da wallafasu.

    Daga karshe, Alhaji Murtala Adewale ya gode wa Gwamnatin Jihar Kano saboda irin goyon baya da taimakon da ta ke bai wa “ya kungiyar tasa,wanda ya ce ya na agaza musu kwarai wajen samun nasara a cikin aikinsu na Jarida.

     

     

     

     

     

     

     

    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Abdullahi Yusuf

      Related Posts

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      December 17, 2025

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      December 16, 2025

      Gidauniyar Bashir Da UNFPA Sun Koyawa Mata 25 Sana,oi A Gusau

      December 15, 2025
      Leave A Reply Cancel Reply

      Top Posts

      Daruruwan Mutane Sun Halarci Jana’izar Ado Lamco, a fadar masarautar Kano

      November 22, 202517

      Kimanin Mata Miliyan 68  Sun Fuskanci Shayi A Najeriya .

      December 10, 202511

      Muna Gabatar Da Sabuwar Jaridarmu Ta Hausa Mai Suna: An zo wajen

      November 14, 202511

      KARIN MAGANARMU NA YAU

      December 8, 20258
      Connect With Us
      • Facebook
      • Twitter
      • Instagram
      • YouTube
      • LinkedIn
      • TikTok
      • Telegram
      • WhatsApp
      Don't Miss
      Tattalin Arziki

      FIDAC Ta Bukaci Kungiyoyin Fararen Hula Su wayar da kan Jamaa akan Sauye-Sauyen Haraji na shekarar 2025 a Najeriya

      By Abbas IbrahimDecember 17, 2025

      Kungiyar tabbatar da da,a da daidaito akan al’amuran kudade da cigaban Al umma wato…

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      December 17, 2025

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      December 16, 2025

      Gidauniyar Bashir Da UNFPA Sun Koyawa Mata 25 Sana,oi A Gusau

      December 15, 2025
      © 2025 ANZO WAJEN. Developed by: ENGRMKS & CO.
      • Home
      • About Us
      • Advertise With Us
      • Contact Us
      • Disclaimer
      • Privacy Policy

      Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.