Close Menu
    Facebook X (Twitter) Instagram
    Facebook X (Twitter) Instagram
    ANZO WAJEN
    Advertise With Us
    Saturday, December 20
    • Shafin Farko
    • Labarai
    • Yanayi
    • Noma

      Kanfanin Dangote Ya Hada Gwiwa Da Abokan Huddarsa Don Bunkasa Noma

      November 25, 2025
    • Ma’adinai
    • Shari’a
    • Siyasa
    • Tattalin Arziki

      FIDAC Ta Bukaci Kungiyoyin Fararen Hula Su wayar da kan Jamaa akan Sauye-Sauyen Haraji na shekarar 2025 a Najeriya

      December 17, 2025
    • Karin Wasu
      1. Addini
      2. Aikata Laifuka
      3. Al’adu
      4. Harkokin Lafiya
      5. Harkokin Tsaro
      6. Harkokin Waje
      7. Ilimi
      8. Jirwaye
      9. Kimiyya Da Fasaha
      10. Kowane Labari
      11. Kwadago
      12. Nishani
      13. Ra’ayi
      14. Rubutun Zube
      15. Sufuri
      16. Yawon Bude Idanu
      17. Wasanni
      18. View All

      Karin Maganarmu Na Yau

      November 15, 2025

      Kwararren Likita Ya Shawarci “Yan Jarida Kan Lafiyar Kwakwalwa

      November 16, 2025

      An Kammala Taron Sanin Makamar Aiki Na Wakilan Kafafan Yada Labarai Na Jihar Kano A Kaduna

      November 16, 2025

      Kanfanin Dangote Ya Hada Gwiwa Da Kamfanin Honeywell Don Fadada Matatar Mai

      November 26, 2025

      Muna Gabatar Da Sabuwar Jaridarmu Ta Hausa Mai Suna: An zo wajen

      November 14, 2025

      Kuncin Rayuwa, Ya Hana Samari Aure

      November 15, 2025

      Aikin Wucin Gadi: Babban Barazana Ga Ci Gaban Dan Adam

      November 15, 2025
    ANZO WAJEN
    Home » 2027:Dungurawa Ya Ce APC Na Bukatar Kwankwaso Don Ta Ci Zabe
    Featured

    2027:Dungurawa Ya Ce APC Na Bukatar Kwankwaso Don Ta Ci Zabe

    Abdullahi YusufBy Abdullahi YusufNovember 21, 2025No Comments1 Views
    images (66)

    2027:Dungurawa Ya Ce APC Na Bukatar Kwankwaso Don Ta Ci Zabe

    Daga Abdullahi Yusuf

    Shugaban Jam’iyyar NNPP reshen Jihar Kano,Alhaji Hashimu Suleiman Dungurawa,ya ce Jam’iyyar APC ta na bukatar Shugaban Kwankwasiyya na duniya baki daya,Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, domin ta ci zaben Shugaban Kasa na shekarar 2027.

    Dungurawa ya ce hakan ya kasance ne kuwa, saboda babu wani Dan Siyasa Mai goyon bayan “Yan Nigeria kamar Sanata Rabiu Kwankwaso.

    Ya yi wannan ikirari ne kuwa yayin da ya ke ganawa da manema labarai a cikin Ofishinsa ranan Al’hamis din da ta wuce.

    “A halin da a ke ciki, Jam’iyyar APC ta rude kuma ta rasa alkibla, saboda haka ta na bukatar wanda zai yi mata jagora domin ta ci Zaben Shugaban Kasa na shekarar 2027,shi ya sanya ta ke neman Jagoranmu,Dakta Rabiu Musa Kwankwaso, da ya zo ya rike mata tuta.

    “Amma Sanata Kwankwaso bai taba neman ya koma APC ba,ita APC din ce da kanta ta ke nemansa da ya dawo cikinta saboda ta gane mahimmancinsa,” in ji Shugaban Jam’iyyar ta NNPP.

    Ya ce hakan ta kasance ne saboda APC ta gaza a wajen mulkin Nigeria tun da ta hau karaga mulki fiye da shekaru goma da su ka wuce.

    “Tun da APC karbi mulkin Nigeria “Yan Kasa su ke ta fama da talauci,tabarbarewar tattalin arziki da kuma rashin tsaro, kuma ta kasa yin maganinsu,” in ji shi.

    Saboda haka, Shugaban Jam’iyyar ta NNPP ya yi kira ga “Yan Nigeria da su yi wo dafifi su karbi Katin Zabe, domin su sami damar zaben Sanata Rabiu Musa Kwankwaso a matsayin Shugaban Kasa a shekarar 2027, domin ya yi maganin wadannan da ma sauran matsalolin da su ke addabarsu.

    Daga nan sai Dungurawa ya yi maraba da Kasafin Kudin shekarar 2026 da ke dauke da kimanin N1.368 tiriliyan, wanda Gwamna Abba Kabir Yusuf ya gabatar wa Majalisar Dokokin Jihar Kano.

    Ya ce, Kasafin Kudin ya kunshi kudire-kudire masu mahimmanci wadanda za su inganta rayuwar Jama’ar Jihar Kano,ciki har da samar da ruwan sha, hanyoyi, kiwon lafiya, harkokin noma,ilimi da kuma tallafa wa mata da matasa.

    Share. Facebook Twitter WhatsApp Telegram
    Abdullahi Yusuf

      Related Posts

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      December 17, 2025

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      December 16, 2025

      Gidauniyar Bashir Da UNFPA Sun Koyawa Mata 25 Sana,oi A Gusau

      December 15, 2025
      Leave A Reply Cancel Reply

      Top Posts

      Daruruwan Mutane Sun Halarci Jana’izar Ado Lamco, a fadar masarautar Kano

      November 22, 202517

      Kimanin Mata Miliyan 68  Sun Fuskanci Shayi A Najeriya .

      December 10, 202511

      Muna Gabatar Da Sabuwar Jaridarmu Ta Hausa Mai Suna: An zo wajen

      November 14, 202511

      KARIN MAGANARMU NA YAU

      December 8, 20258
      Connect With Us
      • Facebook
      • Twitter
      • Instagram
      • YouTube
      • LinkedIn
      • TikTok
      • Telegram
      • WhatsApp
      Don't Miss
      Tattalin Arziki

      FIDAC Ta Bukaci Kungiyoyin Fararen Hula Su wayar da kan Jamaa akan Sauye-Sauyen Haraji na shekarar 2025 a Najeriya

      By Abbas IbrahimDecember 17, 2025

      Kungiyar tabbatar da da,a da daidaito akan al’amuran kudade da cigaban Al umma wato…

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      December 17, 2025

      KARIN MAGANARMU NA YAU:

      December 16, 2025

      Gidauniyar Bashir Da UNFPA Sun Koyawa Mata 25 Sana,oi A Gusau

      December 15, 2025
      © 2025 ANZO WAJEN. Developed by: ENGRMKS & CO.
      • Home
      • About Us
      • Advertise With Us
      • Contact Us
      • Disclaimer
      • Privacy Policy

      Type above and press Enter to search. Press Esc to cancel.